Musayar kalamai sun barke tsakanin fadar shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu, Tinubu ya mayar wa Kwankwaso martani

 Tinubu ya mayar wa Kwankwaso martani





Musayar kalamai sun barke tsakanin fadar shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu, da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar NNPP kuma tsohon gwamanan Kano Sanata Rabi'u Musa kwankwaso kan zargin da kwankwason ya yi na cewar gwamantin Bola ahmed Tinubu na ƙokarin ƙaƙaba dokar ta ɓaci a jihar ta Kano.


Yayin wani taron ƙaddamar da aiki da gwamnatin jiha Kano ta gudanar, an jiyo Kwankwaso na zargin cewa wasu sun hada baki da jagororin jam'iyyar APC suna kokarin fakewa da batun rikicin masarautar Kano su tayar da fitina, don gwamnatin tarayya ta samu damar ƙaƙaba dokar ta ɓaci.


Sai dai Fadar shugaban ƙasar ta yi watsi da zargin da Kwankwason ya yi, tana bayyana shi a matsayin marar tushe ballantana makama.


Musayar kalamai sun barke tsakanin fadar shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu, da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar NNPP kuma tsohon gwamanan Kano Sanata Rabi'u Musa kwankwaso kan zargin da kwankwason ya yi na cewar gwamantin Bola ahmed Tinubu na ƙokarin ƙaƙaba dokar ta ɓaci a jihar ta Kano.


Yayin wani taron ƙaddamar da aiki da gwamnatin jiha Kano ta gudanar, an jiyo Kwankwaso na zargin cewa wasu sun hada baki da jagororin jam'iyyar APC suna kokarin fakewa da batun rikicin masarautar Kano su tayar da fitina, don gwamnatin tarayya ta samu damar ƙaƙaba dokar ta ɓaci.


Sai dai Fadar shugaban ƙasar ta yi watsi da zargin da Kwankwason ya yi, tana bayyana shi a matsayin marar tushe ballantana makama.



Masu sharhi kan al’amuaran yau da kullum dai, na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu inda Farfesa Kamilu Sani Fagge ya ja hankalin gwamnatin tarayya da kuma gwamnatin jihar Kano da cewa su lura da maslahar al’umma.


"A ko ina sai da zaman lafiya ake iya yin komai, bai kamata a ce gwamantin tarayya ko ta jiha su ringa yin abun da za su tunzura al'amarin ba, illa su zama masu samar da masalaha da zaman lafiya a tsakanin al'ummar su" a cewarsa.


Farfesa Kamilu Fagen ya ce kamata ya yi gwamnatin tarayyar da ta jihar Kano, su lura da cewar ko me ake ciki, su ne shugabanin al'umma, kuma hakki ne da ya rataya a wuyansu da su yi jagoranci wajen kiyaye doka da oda", inji shi.


Wannan rikici kan masarautar Kano dai, ta na ci gaba da daukar hankali a sassan Najierya, inda al’amarin ya rage armashin bikin Babbar Sallah a bana, ko da yake Kanawa na ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum tamkar babu wani zaman tankiya a jihar.

Post a Comment

Previous Post Next Post